Mat 10:5-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Su sha biyun nan ne Yesu ya aika, ya yi musu umarni, ya ce, “Kada ku shiga ƙasar al'ummai, ko kuma kowane garin Samariyawa.

6. Sai dai ku je wurin batattun tumakin jama'ar Isra'ila,Irm

7. kuna tafiya, kuna wa'azi, kuna cewa, ‘Mulkin Sama ya kusato.’

8. Ku warkar da marasa lafiya, ku ta da matattu, ku tsarkake kutare, ku kuma fitar da aljannu. Kyauta kuka samu, ku kuma bayar kyauta.

9. Kada ku riƙi kuɗin zinariya, ko na azurfa, ko na tagulla a ɗamararku,

10. kada kuma ku ɗauki burgami a tafiyarku, ko taguwa biyu, ko takalma, ko sanda, don ma'aikaci ya cancanci hakkinsa.

Mat 10