M. Sh 27:16-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. “ ‘La'ananne ne wanda ya raina mahaifinsa ko mahaifiyarsa.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

17. “ ‘La'ananne ne wanda ya ci iyakar maƙwabcinsa.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

18. “ ‘La'ananne ne wanda ya karkatar da makaho daga hanya.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

19. “ ‘La'ananne ne wanda ya yi wa baƙo, ko maraya, ko gwauruwa ta gaske shari'a ta rashin gaskiya.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

20. “ ‘La'ananne ne wanda ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya buɗe fatarin matar mahaifinsa.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

21. “ ‘La'ananne ne wanda ya kwana da dabba.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

22. “ ‘La'ananne ne wanda ya kwana da 'yar'uwarsa, wato 'yar mahaifinsa, ko 'yar mahaifiyarsa.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

23. “ ‘La'ananne ne wanda ya kwana da surukarsa.’“Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’

M. Sh 27