L. Kid 5:16-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Sai firist ya kawo ta kusa, ya tsai da ita a gaban Ubangiji.

17. Ya ɗebo ruwa mai tsarki a cikin kasko, ya kuma ɗauki ƙurar ƙasar da take a alfarwa ta alkawari ya zuba a ruwan.

18. Sa'an nan firist zai kwance gashin kanta, ya sa hadaya ta gari don tunawa a hannuwanta, hadayar gari ce ta kishi. Ya riƙe ruwan nan mai ɗaci da yake kawo la'ana a hannunsa.

19. Sa'an nan zai sa ta ta yi rantsuwa, ya ce mata, “Idan wani mutum bai kwana da ke ba, to, bari ki kuɓuta daga la'anar da ruwan nan mai ɗaci zai kawo.

20. Amma idan kin kwana da wani mutum wanda ba mijinki ba ne,

21. bari Ubangiji ya sa sunanki ya la'antu cikin jama'arki, ya sa cinyarki ta shanye, cikinki kuma ya kumbure.

22. Bari ruwan nan ya shiga cikinki, ya sa cikinki ya kumbure, cinyarki kuma ta shanye.”Sai matar ta amsa, ta ce, “Amin, amin, Ubangiji ya sa ya zama haka.”

23. Firist ɗin zai rubuta waɗannan la'anoni a cikin littafi sa'an nan ya wanke rubutun da ruwan nan mai ɗaci.

24. Ya sa matar ta shanye ruwa wanda yake kawo la'ana, sai ruwan ya shiga cikinta, ya zama la'ana mai ɗaci.

25. Firist kuma zai karɓi hadaya ta gari don kishi a hannun matar, ya kaɗa ta a gaban Ubangiji. Sa'an nan ya kai wurin bagade.

L. Kid 5