Ish 66:7-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. “Tsattsarkan birnina yana kama da uwa wadda ta haifi ɗa, ba tare da naƙuda ba.

8. Ko akwai wanda ya taɓa gani ko ya ji labari irin wannan abu? Ko an taɓa haihuwar al'umma rana ɗaya? Sihiyona ba za ta sha wahala ba kafin a haifi al'umma.

9. Kada ku zaci zan kawo jama'ata a wurin haihuwa in kuma hana ta haihuwa.” Ubangiji ne ya faɗa.

10. Ku yi murna tare da UrushalimaKu yi farin ciki tare da ita,Dukanku da kuke ƙaunar birnin nan!Ku yi murna tare da ita yanzu,Dukanku da kuka yi makoki dominta!

11. Za ku ji daɗin wadatarta,Kamar yaro a ƙirjin mamarsa.

12. Ubangiji ya ce, “Zan kawo muku wadata madawwamiya, dukiyar al'ummai za ta malalo zuwa gare ku kamar kogi wanda ba ya ƙafewa. Za ku zama kamar yaro wanda mahaifiyarsa take renonsa, tana rungume da shi da ƙauna.

13. Zan ta'azantar da ku a Urushalima, kamar yadda uwa take ta'azantar da ɗanta.

Ish 66