Ish 60:20-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

20. Kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.Ni, Ubangiji, zan zama madawwamin haskenki,Mai daɗewa fiye da na rana da na wata.

21. Dukan mutanenki za su yi abin da yake daidai,Za su kuwa mallaki ƙasar har abada.Ni na dasa su, ni na yi suDomin su bayyana girmana ga duka.

22. Har ma da iyalin da suka fi ƙanƙanta da ƙasƙanci,Za su zama babbar al'umma,Kamar al'umma mai iko.Zan sa wannan ya faru nan da nanSa'ad da lokacin da ya dace ya yi.Ni ne Ubangiji!”

Ish 60