10. Ubangiji ya ce wa Urushalima,“Baƙi ne za su sāke gina garukanki,Sarakunansu kuma za su bauta miki.Na hukunta ki da fushina,Amma yanzu zan nuna miki alheri da jinƙai.
11. Ƙofofinki za su kasance a buɗe dare da rana,Domin sarakunan al'ummai su kawo miki dukiyarsu.
12. Amma al'umman da ba su bauta miki ba,Za a hallakar da su.
13. “Itatuwan fir da irinsuMafi kyau daga jejin Lebanon,Za a kawo su domin a sāke gina ki, ke Urushalima,Domin a ƙawata Haikalina,A darajanta birnina.