20. Ya Ubangiji, ka riga ka warkar da ni!Za mu kaɗa garayu mu kuma raira waƙar yabo,Za mu raira yabo cikin Haikalinka muddin ranmu.
21. Haka ya faru bayan da Ishaya ya faɗa wa sarki ya sa curin da aka yi da 'ya'yan ɓaure a kan marurun, ya kuwa warke.
22. Sarki Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan iya zuwa Haikali?”