10. Na zaci a gaɓar ƙarfinaZan tafi lahira,Ba zan ƙara rayuwa ba.
11. Na zaci ba zan ƙara ganin Ubangiji baA wannan duniya ta masu rai,Ko kuwa in ga wani mutum mai rai.
12. An datse raina, ya ƙare,Kamar alfarwar da aka kwance,Kamar saƙar da aka yanke,Na zaci Allah zai kashe ni.
13. Dare farai na yi ta kuka saboda azaba,Sai ka ce zaki yake kakkarya ƙasusuwana.Na zaci Allah zai kashe ni.