1. Gidan sarautar Dawuda kamar itacen da aka sare ne, amma kamar yadda rassa sukan toho daga cikin kututture, haka nan za a sami sabon sarki daga zuriyar Dawuda.
2. Ikon Ubangiji zai ba shi hikima,Da sani, da gwaninta yadda zai mallaki mutanensa.Zai kuwa san nufin Ubangiji, ya kuma yi tsoronsa,
3. Zai ji daɗin yin hidimarsa.Ba zai yi shari'ar ganin ido ko ta waiwai ba.
4. Zai yi wa matalauta shari'a daidai.Zai kuma kāre hakkin masu tawali'u.Bisa ga umarninsa za a hukunta ƙasar,Mugaye za su mutu.