6. Ku gudu don ku tserar darayukanku,Ku gudu kamar jakin jeji.
7. “Kun dogara ga ƙarfinku dawadatarku,Amma yanzu za a ci ku da yaƙi,Kemosh zai tafi bautaTare da firistocinsa dashugabanninsa.
8. Mai hallakarwa zai shiga kowanegari,Don haka ba garin da zai tsira.Kwari da tudu za su lalace,Ni Ubangiji na faɗa.
9. Ku ba Mowab fikafikai,Gama za ta tashi ta gudu,Garuruwanta za su zama kango,Ba mazauna cikinsu.
10. “La'ananne ne shi wanda yake yinaikin Ubangiji da ha'inci,La'ananne ne shi kuma wanda yahana wa takobinsa jini.