Irm 23:19-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Ga shi, hadirin hasalar Ubangiji yataso,Kamar iskar guguwa,Zai tashi a bisa kan mugaye.

20. Ubangiji ba zai huce ba,Sai ya aikata nufin zuciyarsa.Amma sai daga baya za ku ganesarai.”

21. Ubangiji ya ce,“Ni ban aiki waɗannan annabawaba,Duk da haka sun tafi,Ban kuwa yi musu magana ba,Amma sun yi annabci.

22. Amma da a ce sun tsaya cikinshawarata,Da sun yi shelar maganata gajama'ata,Da sun juyar da su daga muguwarhanyarsu,Da mugayen ayyukansu.

23. “Ni Allah na kusa ne kaɗai,Banda na nesa?” In ji Ubangiji.

Irm 23