Irm 23:15-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce a kan annabawa,“Ga shi, zan ciyar da su da abincimai ɗaci,In shayar da su da ruwan dafi.Daga wurin annabawan UrushalimaRashin tsoron Allah ya fito yamamaye dukan ƙasar.”

16. Ubangiji Mai Runduna ya ce wamazaunan Urushalima,“Kada ku kasa kunne ga maganarannabawa,Gama sukan cika kunnuwanku daƙarairayi.Suna faɗar ganin damarsu,Ba faɗar Ubangiji ba.

17. Suna ta faɗa wa waɗanda suke rainamaganar Ubangiji cewa,‘Za ku zauna lafiya!’Ga kowane mai bin nufin tattaurarzuciyarsa,‘Ba masifar da za ta same ka.’ ”

18. Irmiya ya ce, “Gama wane ne a cikin annabawan nan ya taɓa neman shawarar Ubangiji don ya fahimci maganarsa, ko kuwa wane ne ya taɓa kasa kunne don ya ji maganarsa?

19. Ga shi, hadirin hasalar Ubangiji yataso,Kamar iskar guguwa,Zai tashi a bisa kan mugaye.

20. Ubangiji ba zai huce ba,Sai ya aikata nufin zuciyarsa.Amma sai daga baya za ku ganesarai.”

21. Ubangiji ya ce,“Ni ban aiki waɗannan annabawaba,Duk da haka sun tafi,Ban kuwa yi musu magana ba,Amma sun yi annabci.

Irm 23