5. Ubangiji ya ce,“La'ananne ne mutumin da yakedogara ga mutum,Wanda jiki ne makaminsa,Wanda ya juya wa Ubangiji baya,
6. Gama yana kama da sagagi ahamada,Ba zai ga wani abu mai kyau yanazuwa ba.Zai zauna a busassun wurarenhamada,A ƙasar gishiri, inda ba kowa.
7. “Mai albarka ne mutumin da yakedogara ga Ubangiji,Wanda Ubangiji ne madogararsa.
8. Shi kamar itace ne wanda ake dasa abakin rafiWanda yake miƙa saiwoyinsa zuwacikin rafin,Ba zai ji tsoron rani ba,Kullum ganyensa kore ne,Ba zai damu a lokacin fari ba,Ba zai ko fasa yin 'ya'ya ba.
9. “Zuciya ta fi kome rikici,Cuta gare ta matuƙa,Wa zai san kanta?
10. Ni Ubangiji nakan bincike tunani,In gwada zuciya,Domin in sāka wa kowane mutumgwargwadon al'amuransa,Da kuma gwargwadon ayyukansa.
11. “Kamar makwarwar da ta kwantakan ƙwan da ba ita ta nasa ba,Haka yake ga wanda ya sami dukiyarharam,Yana gaɓar ƙarfinsa, za ta rabu dashi,A ƙarshe zai zama wawa.”