15. Kaldiyawa sukan kama mutane da ƙugiya,Sukan jawo su waje da tarunsa,Sa'an nan su tara su cikin ragarsu,Su yi murna da farin ciki.
16. Domin haka sukan miƙa hadaya ga tarunsa,Su ƙona turare ga ragarsu,Domin su ne suka jawo musu wadata, da abinci mai yawa.
17. Za su ci gaba da juye tarunsa ke nan?Su yi ta karkashe al'umman duniya ba tausayi?