Far 18:4-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Bari a kawo ɗan ruwa ku wanke ƙafafunku, ku shaƙata a gindin itace,

5. ni kuwa in tafi in kawo ɗan abinci, don rayukanku su wartsake, bayan haka sai ku wuce, tun da yake kun biyo ta wurin baranku.”Sai suka ce, “Madalla! Ka aikata bisa ga faɗarka.”

6. Ibrahim kuwa ya gaggauta zuwa cikin alfarwa wurin Saratu, ya ce, “Ki shirya mudu uku na gari mai laushi da sauri, ki cuɗa, ki yi waina.”

Far 18