Ezra 4:4-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Sai mutanen ƙasar suka shiga karya zuciyar jama'ar Yahuza, su kuwa suka ji tsoron yin gini.

5. Mutanen kuwa suka yi ijara da mashawarta, da za su sa niyyarsu ta shiririce tun daga zamanin Sairus, Sarkin Farisa, har zuwa zamanin Dariyus, Sarkin Farisa.

6. A farkon sarautar Ahasurus, sai suka rubuta takarda ƙara a kan mazaunan Yahuza, da Urushalima.

7. A zamanin Artashate kuma sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da magoya bayansu suka rubuta wa Artashate Sarkin Farisa takarda da harufan Suriya, aka fassara ta.

8. Rehum shugaban sojoji, da Shimshai magatakarda, suka rubuta takardar ƙara a kan Urushalima zuwa Sarki Artashate.

Ezra 4