Ez 2:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka tashi tsaye, zan yi magana da kai.”

2. Da ya yi magana da ni, sai Ruhu ya sauko a kaina, ya ta da ni tsaye, sa'an nan na ji yana magana da ni.

3. Ya ce mini, “Ɗan mutum na aike ka zuwa wurin jama'ar Isra'ila, al'umma mai tayarwa, waɗanda suka tayar mini. Su da ubanninsu suna yi ta yi mini laifi har yau.

Ez 2