Ez 16:45-60 Littafi Mai Tsarki (HAU)

45. Ke 'yar mahaifiyarki ce wadda ta ƙi mijinta da 'ya'yanta. Ke kuma 'yar'uwar 'yar'uwanki mata ce waɗanda suka ƙi mazansu da 'ya'yansu. Mahaifiyarki Bahittiya ce, mahaifinki kuwa Ba'amore ne.

46. “'Yarki ita ce Samariya wadda take zaune da 'ya'yanta mata wajen arewa da yake. Ƙanwarki ita ce Saduma wadda take zaune kudu da ke tare da 'ya'yanta mata.

47. Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su.

48. “Hakika ni Ubangiji Allah na ce Saduma ƙanwarki da 'ya'yanta mata ba su yi kamar yadda ke da 'ya'yanki mata kuka yi ba.

49. Wannan shi ne laifin Saduma, ƙanwarki, ita da 'ya'yanta mata, suna da girmankai domin suna da abinci a wadace, suna zama a sangarce, amma ba su taimaki matalauta da masu bukata ba.

50. Su masu alfarma ne, sun aikata abubuwa masu banƙyama a gabana, saboda haka na kawar da su sa'ad da na gani.

51. “Samariya ba ta aikata rabin zunubin da kika aikata ba. Abubuwan banƙyama da kika aikata sun sa 'yan'uwanki sun zama kamar adalai.

52. Ke kuma sai ki sha kunyarki, gama kin sa 'yan'uwanki mata su sami rangwamin shari'a saboda zunubanki da kika aikata fiye da nasu, gama gwamma su da ke. Sai ki ji kunya, ki sha ƙasƙancinki, gama kin sa 'yan'uwanki mata su zama kamar adalai.”

53. Ubangiji ya ce wa Urushalima, “Zan komo da Saduma da Samariya da 'ya'yansu mata daga bauta. Sa'an nan zan komo da ke daga bauta tare da su,

54. don ki sha ƙasƙanci saboda abin kunyar da kika aikata. Ƙasƙancinki zai ta'azantar da 'yan'uwanki mata.

55. 'Yan'uwanki mata, wato Saduma da 'ya'yanta mata za su koma kamar yadda suke a dā, Samariya kuma da 'ya'yanta mata za su koma kamar yadda suke a dā. Ke kuma da 'ya'yanki mata za ku koma kamar yadda kuke a dā.

56. Ashe, ba ƙanwarki, Saduma, ta zama abar karin magana a bakinki a kwanakin fariyarki,

57. kafin asirin muguntarki ya tonu ba? Amma yanzu kin zama abin zargi ga 'ya'yan Edom mata, da waɗanda suke kewaye da ita, da 'ya'yan Filistiyawa mata waɗanda suke kewaye, waɗanda suke raina ki.

58. Kina ɗauke da hukuncin lalatarki da na abubuwanki masu banƙyama, ni Ubangiji na faɗa.”

59. “Ni Ubangiji Allah na ce, zan yi miki yadda kika yi, ke da kika yi rantsuwar kafara, kika ta da alkawari.

60. Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin kuruciyarki. Zan ƙulla madawwamin alkawari da ke.

Ez 16