3. “Ubangiji Allah ya ce kaito ga wawayen annabawa waɗanda suke bin ra'ayin zuciyarsu, ba su kuwa ga wani wahayi ba.
4. Ya Isra'ila, annabawanki suna kamar diloli a kufai.
5. Ba ku ƙaura zuwa inda garu ya tsage ba, ba ku gina wa mutanen Isra'ila garu don su kāre kansu a lokacin yaƙi, a ranar Ubangiji ba.
6. Suna faɗar ƙarya, suna kuma yin duban ƙarya, suna cewa, ‘Ubangiji ya ce,’ alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba, duk da haka sun sa zuciya ga cikawar maganarsu.
7. Wahayin ƙarya ne kuka gani, kuna yin duban ƙarya, sa'ad da kuke cewa, ‘Ubangiji ya faɗa,’ ko da yake ni Ubangiji ban faɗa ba.