7. Abin tausayi ne ku da kuke ɓatashari'a,Kuna hana wa mutane hakkinsu.
8. Ubangiji ne ya yi taurarinKaza da 'ya'yantaDa mai farauta da kare.Ya mai da duhu haske,Rana kuwa dare.Shi ya kirawo ruwan teku yabayyana,Ya shimfiɗa shi a bisa ƙasa.Sunansa Ubangiji ne.
9. Ya kawo halaka a kan ƙarfafa,Da a kan birane masu garu.
10. Kun ƙi wanda ya tsaya a kanadalci,Da mai faɗar ainihin gaskiya a gabanshari'a.
11. Kun matsa wa talakawa lamba,Kun ƙwace musu abincinsu.Saboda haka kyawawan gidajen nanda kun gina da dutse,Ba za ku zauna a cikinsu ba,Ba kuwa za ku sha ruwan inabinnanDaga kyawawan gonakin inabinkuba.
12. Na san irin zunuban da kuke yi,Da mugayen laifofin da kuka aikata.Kuna wulakanta mutanen kirki,Kuna cin hanci,Kuna hana a yi wa talakawa shari'aradalci a majalisa.
13. Ashe, ba abin mamaki ba ne,Da masu hankali suka kame bakinsuA waɗannan kwanaki na mugunta.
14. Ku yi ƙoƙari, ku yi nagarta, bamugunta ba,Domin ku tsira.Sa'an nan ne Ubangiji AllahMaɗaukakiZai kasance tare da ku sosai,Kamar yadda kuka ɗauka!
15. Ku ƙi mugunta, ku ƙaunacinagarta,Ku yi adalci cikin majalisaralƙalanku!Watakila Ubangiji Allah MaiRundunaZai yi wa sauran da suka ragu nawannan al'umma alheri.
16. Haka Ubangiji Allah Mai Rundunaya ce,“Za a yi kuka, a yi kururuwa atitunan birninku saboda azaba.Daga ƙauyuka za a kirawomutaneSu zo su yi makokin.Waɗanda suka mutu, tare da masumakoki da aka ijarar da su.
17. Za a yi kuka ko'ina cikin dukangonakin inabinkuGama zan zo in yi muku horo.”