2 Tar 20:26-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. Sai suka taru a kwarin Beraka, wato albarka, a rana ta huɗu, a nan suka yabi Ubangiji. Don haka har wa yau ake kiran wurin, “Kwarin Beraka.”

27. Sai kowane mutumin Yahuza da na Urushalima, tare da Yehoshafat shugabansu, suka koma Urushalima suna murna, gama Ubangiji ya sa su yi farin ciki saboda maƙiyansu.

28. Suka shigo Urushalima da molaye da garayu, da ƙaho zuwa Haikalin Ubangiji.

2 Tar 20