2 Sam 23:1-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Wannan ita ce maganar Dawuda ta ƙarshe. Dawuda ɗan Yesse, shi ne mutumin da Allah ya ɗaukaka, wanda Allah na Yakubu ya zaɓa ya zama sarki, wanda kuma ya shirya waƙoƙin Isra'ila. Dawuda ya ce,

2. “Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina,Saƙonsa yana kan leɓunana.

3. Allah na Isra'ila ya yi magana,Matsaron Isra'ila ya ce mini,‘Sarkin da yake mulkin mutane da adalci,Wanda yake mulki da tsoron Allah,

4. Yana kama da hasken rana a kan girgijen alfijir,Rana da take sa ciyawa ta yi ƙyalƙyali bayan an gama ruwan sama.’

5. “Haka Allah zai sa wa zuriyata albarka,Gama ya yi mini madawwamin alkawari,Duka kuwa a shirye yake, zai kuwa kiyaye.Abin da nake bukata ke nan,Wannan ne nasarata,Na tabbata kuwa Allah zai kammala shi.

6. Amma marasa Allah suna kama da ƙayayuwan da aka zubar,

7. Amma wanda zai taɓa su, sai da wani ƙarfe ko da māshi,Za a ƙone su ƙurmus.”

8. Ga sunayen jarumawan Dawuda, Yosheb-basshebet, daga Takemon, shi ne ɗaya daga cikin shugabanni uku. Ya girgiza māshinsa, ya kashe mutum ɗari takwas baki ɗaya.

24-39. Sauran jarumawan da suka zama talatin sun haɗu da waɗannan,Asahel, ɗan'uwan Yowab,Elhanan, ɗan Dodo, daga Baitalami,Shamma da Elika, daga Harod,Helez, daga Felet,Aira, ɗan Ikkesha, daga Tekowa,Abiyezer, daga Anatot,Sibbekai, daga Husha,Zalmon, daga Aho,Maharai, da Heled, ɗan Ba'ana, daga Netofa,Ittayi, ɗan Ribai, daga Gibeya ta Biliyaminu,Benaiya, daga Firaton,Hurai, daga kwaruruka kusa da Ga'ash,Abiyel, daga Araba,Azmawet, daga Bahurim,Eliyaba, daga Shalim,Yashen, daga Gimzo,Jonatan, ɗan Shamma, daga Harod,Ahiyam, ɗan Sharar, daga Harod,Elifelet, ɗan Ahasbai, daga Ma'aka,Eliyam, ɗan Ahitofel, daga Gilo,Hezro, daga Karmel,Nayarai, daga Arabiya,Igal, ɗan Natan, daga Zoba,Bani, daga Gad,Zelek, daga Ammon,Naharai, (mai ɗaukar wa Yowab, ɗan Zeruya makamai) daga Biyerot,Aira daga Gareb, daga Yattir,Uriya, Bahitte.Dukansu su talatin da bakwai ne shahararrun sojoji.

2 Sam 23