8. “Sa'an nan duniya ta yi tangaɗi, ta girgiza,Harsashin sararin sama ya yi makyarkyata, ya raurawa, saboda fushin Allah.
9. Hayaƙi ya fito daga kafafen hancinsa,Harshen wuta mai cinyewa da garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
10. Ya jā sararin sama baya ya sauko,Da girgije mai duhu a ƙarƙashin ƙafafunsa.
11. Ya hau kerub, ya tashi sama,Ya yi tafiya ta fikafikan iska.
12. Ya rufe kansa da duhu,Gizagizai masu kauri cike da ruwa suna kewaye da shi,
13. Garwashi mai ci daga tsawar walƙiya a gabansa.
14. “Ubangiji ya yi tsawa daga sararin samaAka kuma ji muryar Maɗaukaki.
15. Ya harharba kibau, ya warwatsa magabtansa,Da walƙiyoyin tsawa ya sa su gudu.
16. An bayyana ƙarƙashin teku a fili,An tone tussan duniya,Lokacin da Ubangiji ya yi wa abokan gāba tsautawa,Ya yi musu ruri cikin fushi.
17. Daga Sama Ubangiji ya miƙo ya ɗauke ni,Ya tsamo ni daga zurfafan ruwaye.