2 Kor 12:5-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Zan yi gadara da mutumin nan kam, amma ba zan yi gadara da kaina ba, sai dai ko da raunanata.

6. Ko da zan so yin gadara ma, ba zan zama wawa ba, gama gaskiya zan faɗa. Amma na bar zancen haka, don kada wani ya ɗauke ni fiye da yadda yake ganina, ko yadda yake jin maganata.

7. Don kada kaina yă kumbura kuma saboda mafifitan wahayan da aka yi mini, sai aka saka mini wata cuta, wadda ta zama mini ƙaya, jakadan Shaiɗan, don yă riƙa wahalshe ni, don kada kaina ya kumbura.

8. Sau uku nake roƙon Ubangiji a kan wannan abu ya rabu da ni,

2 Kor 12