1 Tar 15:8-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Daga iyalin Elizafan ɗari biyu, Shemaiya ne shugabansu.

9. Daga iyalin Hebron su tamanin, Eliyel ne shugabansu.

10. Daga iyalin Uzziyel ɗari da goma sha biyu, Amminadab ne shugabansu.

11. Sa'an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyata firistoci, da Lawiyawa, wato Uriyel, da Asaya, da Yowel, da Shemaiya, da Eliyel, da Amminadab,

12. ya ce musu, “Ku ne shugabanni na gidajen kakanninku, Lawiyawa. Sai ku tsarkake kanku da 'yan'uwanku domin ku iya kawo akwatin alkawarin Allah na Isra'ila a inda na shirya masa.

13. Gama Ubangiji Allahnmu ya fashe fushinsa a kanmu saboda ba ku ne kuka ɗauke shi a karo na farko ba, saboda kuma ba mu yi masa sujada kamar yadda aka umarta ba.”

14. Sa'an nan firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji Allah na Isra'ila.

1 Tar 15