1 Sar 10:4-5-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Sai ta ce wa Sulemanu, “Labarin da na ji a ƙasata a kan al'amuranka da hikimarka, gaskiya ne.

7. Amma ban gaskata da labarin ba, sai da na zo na gani da idona, ashe, ko rabi ma ba a faɗa mini ba, gama hikimarka da wadatarka sun fi abin da na ji.

8. Jama'arka, da fādawanka waɗanda suke tsaye a gabanka kullum, sun yi sa'a gama suna jin hikimarka.

9. Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka wanda ya yarda da kai, ya sa ka a kan gadon sarautar Isra'ila, domin Ubangiji yana ƙaunar Isra'ila har abada, ya naɗa ka sarki domin ka zartar da shari'a da adalci.”

1 Sar 10