27. Suna bin su Dawuda kusa kusa, sai manzo ya zo ya ce wa Saul, “Sai ka komo da sauri domin Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
28. Saul kuwa ya koma daga bin Dawuda, ya tafi, ya yi yaƙi da Filistiyawa, domin haka aka riƙa kiran wurin, Sela-hammalekot, wato dutsen tserewa.
29. Dawuda kuwa ya tashi daga can, ya tafi jejin En-gedi inda ya ɓuya.