4. An kakkarya bakunan ƙarfafan sojoji,Amma rarrauna ya zama mai ƙarfi.
5. Ƙosassun mutane suna ƙodago saboda abinci,Masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa.Bakarariya ta haifi 'ya'ya bakwai,Wadda ta haifi 'ya'ya da yawa kuwata rasa su duka.
6. Ubangiji ne yake kashewa, ya kuma rayar,Yana kai mutane kabari,Ya kuma tā da su.
7. Yakan sa waɗansu mutane su zamamatalauta,Waɗansu kuwa attajirai.Yakan ƙasƙantar da waɗansu,Ya kuma ɗaukaka waɗansu.