1 Kor 7:24-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. To, 'yan'uwa, duk halin da aka kira mutum a ciki, sai yă zauna a kai, yana zama tare da Allah.

25. A game da matan da ba su yi aure ba kuwa, ba ni da wani umarnin Ubangiji, amma ina ba da ra'ayina ne a kan ni amintacce ne, bisa ga jinƙan Ubangiji.

26. Na dai ga ya yi kyau mutum yă zauna yadda yake, saboda ƙuncin nan da yake gabatowa.

1 Kor 7