1 Kor 14:35-38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

35. In akwai wani abin da suke so su sani, to, sai su tambayi mazansu a gida, don abin kunya ne mace ta yi magana a cikin taron ikkilisiya.

36. A kanku ne maganar Allah ta fara, ko kuwa a gare ku kaɗai ta isa?

37. In wani yana zato shi annabi ne, ko kuwa mai wata baiwa ta ruhu, to, sai yă fahimta, abin nan da nake rubuto muku umarni ne na Ubangiji.

38. In kuwa wani ya ƙi kula da wannan, shi ma sai a ƙi kula da shi.

1 Kor 14