1 Kor 12:5-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Akwai fanni iri iri na ibada, amma Ubangiji ɗaya ne.

6. Akwai kuma aiki iri iri, amma Allah ɗaya yake iza kowa ga yin kowannensu.

7. An yi wa kowanne baiwa da wani buɗi na Ruhu, don kyautata wa duka.

8. Wani an yi masa baiwa da koyar da hikima ta wurin Ruhu, wani kuma da koyar da sani ta wurin wannan Ruhu.

9. Wani kuwa an yi masa baiwa da bangaskiya ta wurin Ruhun nan, wani kuma baiwar warkarwa ta wurin Ruhun nan,

10. wani kuma yin mu'ujizai, wani kuma annabci, wani kuma baiwar rarrabe ruhu da aljani, wani kuma iya harshe iri iri, wani kuma fassara harsuna.

1 Kor 12