1 Kor 12:17-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Da dukan jiki ido ne, da me za a ji? Da dukan jiki kunne ne, da me za a sansana?

18. Amma ga shi, Allah ya shirya gaɓoɓin jiki, kowaccensu yadda ya nufa.

19. Da dukan jikin gaɓa ɗaya ne, da ina sauran jikin?

20. Amma ga shi, akwai gaɓoɓi da yawa, jiki kuwa ɗaya.

21. Ba dama ido yă ce wa hannu, “Ba ruwana da kai,” ko kuwa kai yă ce wa ƙafafu, “Ba ruwana da ku.”

1 Kor 12