Zak 8:1-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji Mai Runduna kuma ya yi magana da ni, ya ce,

2. “Ni Ubangiji Mai Runduna ina kishin Sihiyona ƙwarai.

3. Zan koma wurin Sihiyona, in zauna a tsakiyar Urushalima. Za a ce da Urushalima birnin gaskiya, da kuma dutsen Ubangiji Mai Runduna, tsattsarkan dutse.

4. Tsofaffi, mata, da maza, za su zauna a titunan Urushalima, kowa yana tokare da sanda saboda tsufa.

5. Samari da 'yan mata zan sa su cika titunan Urushalima, suna wasa.

6. “Idan abin nan ya zama mawuyaci ga sauran jama'a a kwanakin nan, zai zama mawuyacin abu ne a gare ni?

7. Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, zan ceci mutanena daga ƙasar gabas da ƙasar yamma.

Zak 8