19. Sai na ce wa mala'ikan da ya yi magana da ni, “Mene ne waɗannan?”Shi kuwa ya ce mini, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka warwatsa Yahuza, da Isra'ila, da Urushalima.”
20. Sa'an nan kuma Ubangiji ya nuna mini waɗansu maƙera, su huɗu.
21. Sai na ce, “Me waɗannan suke zuwa su yi?”Sai ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka warwatsa Yahuza don kada mutum ya ɗaga kansa. Waɗannan kuwa sun zo don su tsorata su, su karya ƙahonin al'umman duniya waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuza don su warwatsa ta.”