Zab 92:11-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Na ga fāɗuwar maƙiyana,Na ji kukan mugaye.

12. Adalai za su yi yabanyaKamar itatuwan giginya,Za su yi girma kamar itatuwan al'ul na Lebanon.

13. Za su zama kamar itatuwan da aka daddasa a Haikalin Ubangiji,Suna ta yabanya a Haikalin Allahnmu.

14. Waɗanda suke yin 'ya'ya da tsufansu,A kullum kuwa kore shar suke,Suna da ƙarfinsu kuma.

15. Wannan ya nuna Ubangiji adali ne,Shi wanda yake kāre ni,Ba kuskure a gare shi.

Zab 92