11. Wa ya san iyakar ikon fushinka?Wa ya san irin tsoron da hasalarka za ta kawo?
12. Ka koya mana mu sani ranmu na ɗan lokaci ne,Domin mu zama masu hikima.
13. Ya Ubangiji, sai yaushe za ka ji tausayinmu?Ka ji tausayin bayinka!
14. Ka cika mu da madawwamiyar ƙaunarka a kowace safiya,Don mu raira waƙoƙin murna dukan kwanakin ranmu.