Zab 88:8-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Ka sa abokaina su yashe ni,Ka sa sun ware ni.An kange ni, ba yadda zan kuɓuta.

9. Idanuna sun raunana saboda wahala.Ya Ubangiji, kowace rana ina kira gare ka,Ina ta da hannuwana zuwa gare ka da addu'a!

10. Kakan yi wa matattu mu'ujizai ne?Sukan tashi su yabe ka?

11. Akan yi maganar madawwamiyar ƙaunarka a kabari?Ko amincinka a inda ake hallaka?

Zab 88