6. Sukan taru a ɓoye,Suna kallon duk abin da nake yi.Suna sa zuciya za su iya kashe ni.
7. Ka hukunta su, ya Allah saboda muguntarsu,Da fushinka ka kori waɗannan mutane!
8. Ka san irin wahalar da nake sha,Kana riƙe da lissafin yawan hawayena.Ashe, ba a rubuce suke a littafinka ba?