16. Amma ina kira ga Allah, yă taimake ni,Ubangiji kuwa zai cece ni.
17. Koke-kokena da nishe-nishenaSuna hawa zuwa gare shi da safe, da tsakar rana, da dad dare,Zai kuwa ji muryata.
18. Zai fisshe ni lafiyaDaga yaƙe-yaken da nakan yi da magabtana masu yawa.
19. Allah, shi wanda yake mulki tun fil azal,Zai ji ni, zai kore su.Ba abin da suka iya yi a kai,Domin ba su tsoron Allah.
20. Abokina na dā,Ya yi wa abokansa faɗa,Ya ta da alkawarinsa.