Zab 55:16-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Amma ina kira ga Allah, yă taimake ni,Ubangiji kuwa zai cece ni.

17. Koke-kokena da nishe-nishenaSuna hawa zuwa gare shi da safe, da tsakar rana, da dad dare,Zai kuwa ji muryata.

18. Zai fisshe ni lafiyaDaga yaƙe-yaken da nakan yi da magabtana masu yawa.

19. Allah, shi wanda yake mulki tun fil azal,Zai ji ni, zai kore su.Ba abin da suka iya yi a kai,Domin ba su tsoron Allah.

20. Abokina na dā,Ya yi wa abokansa faɗa,Ya ta da alkawarinsa.

Zab 55