Zab 44:5-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. Da ikonka muka kori abokan gābanmu,Saboda kasancewarka tare da muMuka rinjayi magabtanmu.

6. Ban dogara ga bakana ba,Takobina kuwa ba zai cece ni ba.

7. Amma ka cece mu daga abokan gābanmu,Ka kori waɗanda suke ƙinmu.

8. Za mu yabe ka kullum,Mu yi maka godiya har abada.”

9. Amma yanzu, ya Allah, ka yashe mu,Ka bari aka kore mu,Ba ka ƙara fita ka yi tafiya tare da sojojinmu ba.

Zab 44