Zab 38:7-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Ina fama da zazzaɓi,Ina rashin lafiya ƙwarai.

8. An ragargaza ni sarai, an kuwa ci nasara a kaina,Na damu a zuciyata, ina nishi don zafi.

9. Ka san bukatata, ya Ubangiji,Kana jin dukan nishe-nishena.

10. Zuciyata tana ɗar, ƙarfina ya ƙāre,Idanuna sun dushe.

11. Abokaina da maƙwabtana ba su ko zuwa kusa da ni, saboda miyakuna,Har iyalina ma sun guje mini.

Zab 38