7. Ina fama da zazzaɓi,Ina rashin lafiya ƙwarai.
8. An ragargaza ni sarai, an kuwa ci nasara a kaina,Na damu a zuciyata, ina nishi don zafi.
9. Ka san bukatata, ya Ubangiji,Kana jin dukan nishe-nishena.
10. Zuciyata tana ɗar, ƙarfina ya ƙāre,Idanuna sun dushe.
11. Abokaina da maƙwabtana ba su ko zuwa kusa da ni, saboda miyakuna,Har iyalina ma sun guje mini.