Zab 32:9-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Kada ka zama wawa kamar doki ko alfadari,Wanda dole sai da linzami, da ragama za a sarrafa shi,Sa'an nan yă yi maka biyayya.”

10. Tilas ne mugu yă sha wahala,Amma masu dogara ga Ubangiji,Madawwamiyar ƙaunarsa tana kiyaye su.

11. Dukanku adalai, ku yi murna,Ku yi farin ciki,Saboda abin da Ubangiji ya yi!Dukanku da kuke yi masa biyayya,Ku yi sowa ta farin ciki!

Zab 32