Zab 17:1-3 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ka kasa kunne ga roƙona, ni adalin mutum,Ka lura da kukana na neman taimako!Ka kasa kunne ga addu'ata,Gama ni ba mayaudari ba ne.

2. Za ka shara'anta shari'ar da za ta gamshe ni,Saboda ka san abin da yake daidai.

3. Ka san zuciyata,Kakan zo gare ni da dare,Ka riga ka jarraba ni sarai,Ba ka kuwa sami mugun nufi a cikina ba.Na ƙudurta kuma bakina ba zai yi saɓo ba.

Zab 17