Zab 11:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Na dogara ga Ubangiji domin zaman lafiya,Wauta ce idan kun ce mini,“Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu,

2. Domin mugaye sun ja bakkunansu,Sun kuma ɗana kibansuDomin su harbi mutanen kirki a duhu.

3. Ba abin da mutumin kirki zai iya yiSa'ad da kome ya lalace.”

4. Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa,Yana da kursiyinsa a Sama.Yana kallon dukan mutaneYana sane da abin da suke yi.

5. Yana auna masu kirki da mugaye dukka,Yana ƙin marar bin doka gaba ɗaya.

Zab 11