Zab 105:3-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Ku yi murna saboda mu nasa ne,Ku yi murna dukanku da kuke bauta wa Ubangiji!

4. Ku je wurin Ubangiji neman taimako,Ku tsaya a gabansa koyaushe.

5-6. Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim,Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu,Ku tuna da mu'ujizansa masu girma, masu banmamaki,Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke.

7. Shi Ubangiji, shi ne Allahnmu,Umarnansa domin dukan duniya ne.

8. Zai cika alkawarinsa har abada,Alkawaransa kuma don dubban zamanai,

9. Yarjejeniyar da ya yi da Ibrahim,Da alkawarin da ya yi wa Ishaku.

Zab 105