26. Sai ya aiki bayinsa Musa da Haruna, waɗanda ya zaɓa.
27. Suka aikata manya manyan ayyuka na Allah,Suka kuma yi ayyukan al'ajabi a Masar.
28. Ya aika da duhu a bisa ƙasar.Musa da Haruna ba su tayar wa umarnansa ba.
29. Ya mai da ruwan kogunansu su zama jini,Ya karkashe kifayensu duka.
30. Ƙasarsu ta cika da kwaɗi,Har a fādar sarki.
31. Allah ya ba da umarni, sai ƙudaje da ƙwariSuka cika dukan ƙasar.
32. Ya aiki ƙanƙara da tsawa a bisa ƙasarsuMaimakon ruwan sama.
33. Ya lalatar da 'ya'yan inabinsu da itatuwan ɓaurensu,Ya kakkarya itatuwansu.
34. Ya ba da umarni, sai fāri suka zo,Dubun dubbai da ba su ƙidayuwa.