1. Waƙata ta aminci ce da gaskiya.Ina raira maka ita, ya Ubangiji.
2. Abin da nake yi ba zai zama laifi ba,Yaushe za ka zo wurina?Da zuciya mai tsabta zan zauna a gidana.
3. Ba zan jure da mugunta ba ko kaɗan.Na ƙi jinin ayyukan waɗanda suka bijire wa Allah,Ba ruwana da su.