Zab 10:4-8 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Mugun mutum da girmankansa yana cewa, “Ba Allah!”Wannan ne abin da mugu yake tunani.

5. Yakan yi nasara a dukan abin da yake yi.Ba zai fahimci hukuncin Allah ba,Yana yi wa abokan gābansa duban raini.

6. Yana ce wa kansa “Ba zan taɓa fāɗuwa ba,Ba zan taɓa shan wahala ba.”

7. Maganganunsa suna cike da zage-zage, da ƙarairayi, da barazana,Yana da saurin faɗar maganganun ƙiyayya da na mugunta.

8. Yakan ɓuya cikin ƙauyuka,Yă jira a can har yă kashe marasa laifi.Yakan yi sanɗa, ya kama kāsassu,

Zab 10