Yush 7:6-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Zukatansu suna ƙuna da ƙullaƙulle kamar tanderu.Fushinsu na ci dare farai,Da safe fushinsu yana ci bal-bal kamar harshen wuta.

7. “Dukansu suna da zafi kamar tanderu.Suna kashe masu mulkinsu.Dukan sarakunansu sun faɗi.Ba wanda ya kawo mini kuka.”

8. Ubangiji ya ce, “Mutanen Ifraimu sun haɗa kansu da al'ummai,Sun zama kamar wainar da ba a juya ba.

9. Baƙi sun cinye ƙarfinsu, su kuwa ba su sani ba,Furfura ta faso musu, amma ba su sani ba.

Yush 7