13. “Sa'ad da Ifraimu ta ga ciwonta,Yahuza kuma ta ga rauninta,Sai Ifraimu ta aika zuwa Assuriya,Wurin babban sarki.Amman ba zai iya warkar da ciwonki, ko rauninki ba.
14. Zan zama kamar zaki ga Ifraimu,Kamar sagarin zaki ga mutanen Yahuza.Ni kaina zan yayyage, in yi tafiyata.Zan ɗauka, in tafi, ba wanda zai yi ceto.